1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hankoron neman zaman lafiya

September 6, 2013

Shirin telebijin don neman fahimtar juna da zaman lafiya ta amfani da littattafai masu tsarki na addinan Kirista da Musulunci ba tare da daga murya ba.

https://p.dw.com/p/19d4q
Zum Thema: Amnestie für Boko Haram, 19. Juni 2013. George Ehusani, Leiter der Stiftung „Lux Terra“. Titel: DW_ Nigeria_Boko-Haram4: Schlagworte: George Ehusani, Stiftung „Lux Terra“, Boko Haram Wer hat das Bild gemacht/Fotograf / Copyright: Katrin Gänsler Wann wurde das Bild gemacht?: 06. Juni 2013 Wo wurde das Bild aufgenommen?: Abuja, Nigeria
Hoto: Katrin Gänsler

A wannan makon ma jaridun na Jamus sun rubuta labarai da dama game da nahiyarmu ta Afirka, daga ciki har da neman zaman lafiya a arewacin Najeriya da aikin hakar zinari a Afirka ta Kudu.

A labarinta mai taken hankoron neman zaman lafiya jaridar Die Tageszeitung ta ce mace-mace da ayyukan tarzoma sun mamaye kanun labaru, to amma mabiya addinan Kirista da Musulunci a arewacin Najeriya na koyan darasi daga juna musamman don neman zaman lafiya.

"Tashar telebijin mai zaman kanta ta AIT mai shelkwata a Abuja tana watsa wani shiri mai taken Dandalin addini ko kuma "Interfaith Forum" sau biyu a mako da ke kokarin kawar da bambamci tsakanin Kirista da Musulmi. Kimanin mutane miliyan 50 ke kallon wannan shiri inda ake tattaunawa tsakanin Prista George Ehusani da kuma Imam Muhammad Nuruddeen Lemu. Wannan dandalin na amfani da ayoyi daga littattafai masu tsarki na addinan biyu ba tare da daga murya ba, inda suke kira ga samun fahimtar juna. Wannan salon na tattaunawa ko yin sulhu tsakanin addini wani abin yabawa ne musamman a arewacin Najeriya me fama da rikicin addini da na kabilanci, inda kuma ayyukan ta'addanci na kungiyar nan da ake wa lakabi da Boko Haram ya kara jefa yankin cikin mawuyacin hali na rashin tsaro."

Yajin aiki ya kawo cikas ga tattalin arziki

Wani sabon yajin aikin gama gari ya jefa gwamnatin Afirka ta Kudu karkashin jagorancin ANC cikin halin na tsaka mai wuya, inji jaridar Frankfurter Allgemeine Zeitung sannan sai ci gaba kamar haka.

Members of the National Union of Mine (NUM) take part in a strike in the central business district area of Johannesburg, August 27, 2013. South Africa's petrol station and car dealership workers on Tuesday announced a strike for higher wages next week, signalling more labour disruption to a struggling economy also facing stoppages in gold mines. Africa's largest economy is facing a wave of wage increase demands and strikes by increasingly militant workers, renewing a challenge to President Jacob Zuma after violent mines strikes last year dented growth and led to sovereign credit downgrades. REUTERS/Ihsaan Haffejee (SOUTH AFRICA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST ENERGY BUSINESS EMPLOYMENT) SOUTH AFRICA OUT. NO COMMERCIAL OR EDITORIAL SALES IN SOUTH AFRICA, eingestellt von haz
Hoto: Reuters

"Tattalin arzikin Afirka ta Kudu ya fuskanci koma baya sakamakon yajin aikin gama gari da ma'aikata a kamfanoni da dama ciki har na motoci da mahaka zinari ke yi. A ranar Talata ma'aikata hako zinari kimanin dubu 80 sun ajiye aikinsu suna masu neman karin albashi. Sai dai kamfanonin sun ce ba za su iya biya wa ma'aikatan bukatunsu ba, domin a cewarsu sun yi rauni sakamakon wasu yaje-yajen aikin da aka yi a wasu bangarorin hakan ma'adanan karkashin kasa. Ko da yake an cimma wani kwarkwaryan daidaito a ranar Laraba da rana amma har yanzu da sauran aiki a gaba. Ko da yake Afirka ta Kudu ke samar da kashi daya bisa uku na zinari a duniya, amma kamfanonin hakan wannan arziki sun yi rauni, kuma sai an yi hako mai zurfin gaske karkashin kasa kafin a cimma wani abin kirki, wanda haka ke kara yawan kudin da aka kashewa wajen tafiyar da aikin."

Yaki ya daidaita gabacin Kongo

A child stands in front of Indian soldiers of the UN mission in the Democratic Republic of Congo (MONUSCO) driving an armoured vehicle at the border zone in Kagnaruchinya, 7 km north of Goma, on June 2, 2013. The M23 rebellion -- launched by Tutsi former soldiers who mutinied in April 2012 -- is the latest in years of violence that have ravaged the vast central African country's mineral-rich east. A peace deal signed in February by 11 regional countries had brought relative calm until it was broken in the three days leading up to Ban's visit. The two sides stopped fighting while the UN leader toured the flashpoint city of Goma. AFP PHOTO/Junior D. Kannah (Photo credit should read Junior D. Kannah/AFP/Getty Images) Erstellt am: 02 Jun 2013
Hoto: Junior D. Kannah/AFP/Getty Images

Ita kuwa jaridar Neue Zürcher Zeitung labari ta buga a kan abin da ta kira nasarar da Majalisar Dinkin Duniya ta samu a Kongo-Kinshasa tana mai cewa sojojin duniya na amfani da sabon kudurin Kwamitin Sulhu suna fatattakar 'yan tawaye, sannan sai ta kara da cewa.

"Bayan shekaru masu yawa tana zura ido ba tare shiga yakin ba, yanzu kan Majalisar Dinkin Duniya tana fada gadan-gadan a gabacin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo. Kungiyoyin 'yan tawaye masu gaba da juna musamman kungiyar M23 sun daidaita yankin na gabacin Kongo. Ita kuma rundunar kiyaye zaman lafiya ta Monusco mai sojoji dubu 19, tana samun nasara tun bayan fadada aikinta a cikin makonnin da suka gabata. Sai dai masu sanya ido a kan abin da ka je ya komo ba su hango lokacin kawo karshen rikicin nan gaba kadan ba.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe