1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Har yanzu Mali na cikin rikici

Usman Shehu UsmanApril 16, 2015

Ƙasar Mali an samu asarar rayuka bayan harin da aka kai wa sojojin rundunar MINUSMA ta Majalisar Ɗinkin Duniya hari lafiya inda aƙalla mutane uku suka mutu kana wasu 16 suka jikkata.

https://p.dw.com/p/1F6o4
Mali Polizeiabsperrung bei Bamako
Hoto: AFP/Getty Images/I. Sanogo

Wani ɗan kunar bakin wake dai ya tarwaza kansa a sansanin sojojin Majalisar Ɗinkin Duniya, inda ya kashe fararen hula uku. Kana wasu kimanin 16 suka jikkata. Akasarin wadanda aka jikkatan ma'aikata masu aikin kiyaye zaman lafiya ne. An yi kiyasin jami'ai kimanin dubu 10000, ke a sansanin na MDD a Mali, inda suke aikin dawo da doka da oder a ƙasar, tun bayan da 'yan ta'addan Al-Qaida suka rikita ƙasar a shekra ta 2012.