1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-hare a garin Gao na kasar Mali

October 7, 2013

Rahotanni daga kasar Mali na cewar da sanyin safiyar yau an kai hare-hare na bam a garin Gao da ke arewacin kasar wanda ya yi sanadiyyar lalata gine-gine da jikkata wani soja.

https://p.dw.com/p/19vXi
Militiaman from the Ansar Dine Islamic group, who said they had come from Niger and Mauritania, ride on a vehicle at Kidal in northeastern Mali, June 16, 2012. The leader of the Ansar Dine Islamic group in northern Mali has rejected any form of independence of the northern half of the country and has vowed to pursue plans to impose sharia law throughout the West African nation. Iyad Ag Ghali's stance could further deepen the rift between his group and the separatist Tuareg rebels of the National Movement for the Liberation of Azawad (MNLA) as both vie for the control of the desert region. Picture taken June 16, 2012. REUTERS/Adama Diarra (MALI - Tags: POLITICS CIVIL UNREST CONFLICT RELIGION TPX IMAGES OF THE DAY)
Hoto: Reuters

Mai magana da yawun rundunar hadin gwiwa ta sojin Mali da Faransa wanda suka yi aiki fatattakar masu kaifin kishin addini a Mali din ya ce garin Gao da ke arewacin kasar ya fuskancin hare-hare na bam a karon farko cikin watanni da dama.

Jami'in mai suna Hubert de Quievrecourt ya ce kimanin bam biyar aka jefa da sanyin safiyar yau a garin na Gao wanda biyu daga cikinsu suka fada wata unguwa ta fararen hula.

Kawo yanzu dai babu wani wani labarin asarar rayuka da aka samu sai dai mai Mr. Quievrecourt ya ce sojan gwamnatin Mali daya ya jikkata.

Ya zuwa yanzu dai babu wata kungiya da ta dau alhakin kai harin sai dai mabiya kungiyar nan ta Al-Qaida a watannin da suka gabata sun karbe iko da garin kafi daga bisani a fatatake su.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammed Awal Balarabe