1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-hare a garin Kumo na jihar Gombe

June 26, 2013

An ji karar harbe-harbe da fashewar abubuwa a Kumo da ke Gombe, a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

https://p.dw.com/p/18weu
Nigeria police detain suspicious people April 28, 2011 near a polling station during a security operation to stave ballot box-snatching in Bauchi, the capital of Bauchi state, nothern Nigeria.Two Nigerian states hit hard by deadly riots after presidential elections went back to the polls for governor races Thursday amid a security lockdown and with scores still displaced. Soldiers accompanied electoral officials to polls in Kaduna and Bauchi states and the electoral commission scrambled to find some 2,000 workers to replace those who refused to show up because of fears of violence. Police and military personnel in armoured vehicles patrolled the streets of Kaduna city, the capital of the same state, and set up roadblocks to search cars. Police kept a close eye on Bauchi city, the capital of that state. AFP PHOTO / Tony KARUMBA (Photo credit should read TONY KARUMBA/AFP/Getty Images)
Hoto: Tony Karumba/AFP/Getty Images

An kwashe daren jiya ana jin karar harbe-harbe da fashewar wasu abubuwa masu karfi da ake zaton bama-bamai ne, bayan wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai garin Kumo mai nisan kilomita 50 daga Gombe fadar gwamnatin jihar Gombe dake Arewa maso gabashin Najeriya.Tun da misalin karfe 11 na daren jiyan ne dai mazauna garin Kumon suka fara jin karar harbe-harbe, tare da muryoyi dake yin kabbara. Wasu dake makobtaka da ofishin ‘yan sanda na garin suka ce an kai hari a ofishin ‘yan sanda.

Sai dai babu wani cikakken bayani kan wadanda wadannan hare-hare ya rutsa da su saboda cikin dare abin ya faru. Wannan dai shi ne karo na farko da aka kai irin wannan hari a yankin, wanda a baya ke karkashin dokar-ta-bacin da shugaba Jonathan na Najeriya ya ayyana a jihohin Borno da Yobe da Adamawa. Ya zuwa yanzu dai babu wata sanarwa da hukumomin suka bayar kan wadannan hare-hare inda kuma babu wata Kungiya da ta dauki alhakin kai hare-haren.

Mawallafi : Al-Amin Suleiman Muhammad
Edita        : Saleh Umar Saleh