Hare-hare a Iraki sun hallaka mutane 15
July 14, 2013Talla
Wani dan sanda da ya roki a sakaya sunansa ya ce an kai hare-haren ne gabannin lokacin buda baki a kasar, lamarin da ya yi sanadiyyar rasuwar mutane biyar a Nasiryyah da wasu hudu a Karbala yayin da mutane shidda su ka gamu da ajalinsu a Musayyib.
Baya ga wannan, jami'an sun ce harin na yau ya girgiza garin Kut da Basra sai dai kawo wannan lokacin ba a tantance wadanda su ka rasu ko jikkata ba.
Jama'a da dama a kasar dai na ta dari-dari dangane da yawaitar hare-hare makamantan wannan, inda wasu ke tunanin kasar ka iya komawa yakin basasa da ta tsinci kanta a ciki a shekarun 2006 da 2007.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Zainab Mohamed Abubakar