1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-hare a kan wani asibiti a Libiya

Abdourahamane HassaneJune 12, 2016

Mutane uku suka mutu kana wasu bakwai suka jikkata a cikin wani harin kunar bakin wake da aka kai a kan wani asibitin da ke a birnin Syrte na Libiya.

https://p.dw.com/p/1J5OT
Libyen Anschlag in Tripoli
Hoto: Reuters/H. Amara

Majiyoyin tsaro sun ce harin ya yi kaca-kace da asibitin tare da haddasa asara mai yawan gaske.Sojojin masu yaki da Kungiyar IS wadanda galibinsu 'yan asilin garin Misirata ne da ke a yankin yammancin Libiyar na kalubalantar masu kai harin kunar bakin wake na Kungiyar IS.

Kuma kawo yanzu an kashe 120 daga cikin sojojin yayin da wasu 500 suka jikkata. a sumamen da Kungiyar IS ta ke kai musu ba dare ba rana.