1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-haren kunar bakin wake a Chadi

Ahmed SalisuDecember 5, 2015

Rahotanni daga Chadi na cewar wasu hare-hare bam da aka kai sun yi sanadin rasuwar mutane akwalla 27 a wata kasuwa da ke tsibirin Loulou Fou.

https://p.dw.com/p/1HI2T
Doppelanschlag in Tschad
Hoto: Reuters/M. Ngarmbassa

Shaidun gani da ido sun bayyanawa kamfanin dillancin labarai na AP cewar baya ga wanda suka rasu din, wasu da suka kai 90 sun samu raunuka, wasunsu ma munana.

Mai magana da yawun rundunar 'yan sanda Chadi din a wajen da wannan hari ya wakana ya ce wasu mata ne uku dauke da bama-bamai suka kai harin.

Ya zuwa yanzu dai babu wata kungiya da ta dau alhakin kai wannan harin, sai dai kungiyar nan ta Boko Haram ta kai jerin hare-hare a Chadi din don ko a watan jiya ma sai da wata 'yar kunar bakin wake ta hallaka mutane 3 a wani kauye dab da tafkin Chadi.