1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-haren sun hallaka jami'in diplomasiya na Iran

November 19, 2013

Hare-haren kunar bakin sun hallaka mutane 23 kusan da ofishin jadancin Iran a Lebanon

https://p.dw.com/p/1AKni
Hoto: Reuters

Jami'in diplomasiya na kasar Iran na cikin mutane 23 da suka hallaka sanadiyar tagwayen hare-haren kunar bakin wake, kusa da ofishin jakadancin kasar ta Iran da ke Beirut babban birnin kasar Lebanon. Akwai wasu mutane kimanin 150 da suka samu raunika.

Jakada Ghazanfar Roknabadi ya tabbatar da mutuwar Ibrahim Ansari jami'in diplomasiya, bayan hare-haren bama-bamai da aka kai da mota da kuma babur.

Tuni mahukuntan birnin Teheran na Iran suka zargi Isira'ila da hannu cikin farmakin.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Umaru Aliyu