1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari a kudancin jihar Bornon Najeriya

Al-Amin Sulaiman Muhammad/Ahmed SalisuNovember 30, 2014

Ana fargabar mutane da dama sun rasu sakamakon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a garin Shani da ke kudancin jihar Bornon Najeriya.

https://p.dw.com/p/1DxCH
Nigeria Boko Haram Terrorist
Hoto: picture alliance/AP Photo

Wakilinmu na Gombe Al-Amin Sulaiman Muhammad da ke bin diddigin labarin ya ce wadan suka tsira daga wannan hari sun bayyana cewa a daren jiya ne Asabar ce ‘yan bindigar suka afkawa garin dauke da muggan makamai da kuma bama-bamai inda suka bude wuta kan mutane ba kakkautawa.

Baya ga wanda maharan suka hallaka, a hannu guda sun kuma kona gidaje da ababan hawa da dama lamarin da ya tilasta mutane shiga cikin dazuka da garuruwa makota. Ya zuwa yanzu dai hukumomi ko jami'an tsaro ba su kai ga cewa komai kan harin ba.