Harin bam ya hallaka mutune 40 a Jimeta
June 5, 2015A tarayyar Najeriya akalla mutane 40 suka hallaka a yammacin jiya Alhamis a sakamakon tashin bam a tsakiyar wata kasuwar birnin Jimeta fadar Jihar Adamawa a yankin Arewa masu gabashin kasar.
Bam din dai ya tashi dab da inda cunkoson jama'a ya ke yayin harkokin kasuwa da zirga-zirgar jama'a a bakin kasuwar, lamarin da ya haddasa mutuwar mutanen dama jikkatar wasu masu yawan gaske. Ana kuma fargabar karuwar salwantar rayuka.
Tuni dai Gwamnan jihar ta Adamawa Muhammad Umaru Jibrilla, ya bayyana kaduwa game da wannan lamarin da ke zama karon farko a jihar, kuma kwanaki kalilan da hawansa karaga.
Kawo yanzu dai babu wani ko wata kungiya da ta dauki alhakin kai wannan hari .Sai dai harin na kama da irin wanda kungiyar Boko Haram ta saba kaiwa a wannan yanki na Arewa maso gabashin kasar ta Najeriya.