1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin bam ya kashe mutane huɗu a Jos

May 25, 2014

An ba da rahoton cewar an sake samun tashi bam a birnin Jos fadar gwamnatin jihar Filato da ke a Najeriya wanda a ciki mutane guda huɗu suka mutu.

https://p.dw.com/p/1C6VD
Anschlag in Jos, Nigeria
Hoto: picture alliance / AP Photo

Masu aiko da rahotannin sun ce mutumin da ya kai harin ya samami wasu jama'ar ne da ke kalon wasannin ƙwalon ƙafa na gasar nahiyar Turai.

Maharin ya matso da motarsa a kusa da tarin jama'ar, to sai dai bam ɗin ya fashe kafin ya isa a wurinsu. Wannan harin bam dai na zuwa ne kwanaki 4 da tashin wasu tagwayen bama-bamai a garin na Jos, waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 200.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe