1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Taliban ta kai hari a ofishin jakadancin Turkiya

Lateefa Mustapah Ja'afarFebruary 26, 2015

Wani harin kunar bakin wake da aka nufi kaiwa a kan ofishin jakadancin kasar Turkiya da ke kusa da ofishin jakadancin Iran a kasar Afghanistan ya hallaka mutane biyu.

https://p.dw.com/p/1Ei2O
Hoto: Reuters/Mohammad Ismail

Rahotanni sun nunar da cewa tuni kungiyar Taliban ta dauki alhakin kai harin bam din da ya tashi a kofar ofishin jakadancin Iran, inda ta ce ta kudiri kai harin ne a kan ayarin motocin wasu 'yan kasashen ketare. Mataimakin ministan cikin gida na kasar ta Afghanistan Mohammad Ayub Salangi ya tabbatar da faruwar al'amarin. Jami'an 'yan sandan kasar sun ce daya daga cikin wadanda suka rasa rayukansu dan kasar Turkiya ne kana gudan kuma dan Afghanistan din ne da ya zo wucewa.