1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kunar bakin wake a birnin Jeddah

Salissou BoukariJuly 4, 2016

Wani dan kunar bakin wake ya hallaka kansa, ya kuma raunata wasu jami'an tsaro biyu kusa da karamin ofishin jakadancin Amirka a birnin Jeddah na kasar Saudiyya.

https://p.dw.com/p/1JIV4
Saudi-Arabien Selbstmordanschlag nahe US-Konsulat in Dschidda
Hoto: Getty Images/AFP

Harin dai ya wakana da daren ranar Lahadi wayewar wannan Litinin, inda dan kunar bakin waken ya ajiye motarsa a gaban wani babban asibiti da ke kallon karamin ofishin jakadancin na Amirka a birnin Jeddah, kuma ya tashi bam din da ke ciki a daidai lokacin da jami'an tsaron biyu suka zo domin bincikensa a cewar wata majiya ta jami'an tsaro. Gidan talbijin din kasar ta Saudiyya ya tabbatar da wannan hari, inda masu bincike ke kokarin tantance gawar wanda ya kai harin.