1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hatsari ya auku a wata mahaƙar ma'adanai a Gini

November 22, 2013

masu hakar ma'adanai 12 sun hallaka sanadiyyar zabtarewar ƙasa da ta faru a yankin arewa maso gabashi na ƙasar.

https://p.dw.com/p/1AMjG
Achtung: Nicht vor dem 28.08.2013 veröffentlichen! Quelle: http://multimedia.hrw.org/distribute/bshjqanvug Tanzania: Hazardous Life of Child Gold Miners Government, World Bank, Donors Should Address Child Labor in Mines Two 13-year-old boys and one 15-year-old boy pour crushed gold ore over a sisal sack to concentrate the particles of gold at a processing site in Mbeya Reigon, Tanzania. © 2013 Justin Purefoy for Human Rights Watch.
Hoto: HRW/Justin Purefoy

Aƙalla musu haƙar ma'adanai 12 ta hanyar da ta saɓa wa ƙa'ida, suka hallaka yayin da wasu masu yawa suka yi ɓatan dabo sakamakon zabtarewar ƙasa da aka samu cikin yankin arewa maso gabashin ƙasar Gini Conakry. Wasu majiyoyin tsaro da mazauna yankin sun shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, lamarin ya faru cikin daren ranar Talata da ta gabata a garin Siguiri. Shaidun gani da ido sun ce an ci gaba da gudanar da ayyukan ceto har zuwa wannan Alhamis da ta gabata.Ƙasar ta Gini Conakary da ke yankin yammacin Afirka tana cikin ƙasashen masu ma'adanan ƙarƙashin ƙasa kamar zinare da lu'ulu'u, amma galibin al'ummar ƙasar suna rayuwar hannu-baka hannu-ƙwarya.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Abdourahamane Hassane