1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hosni Mubarak ya musunta kashe masu zanga-zanga

August 13, 2014

Tsohon shugaban ƙasar Masar wanda ya bayyana a gaban kotu ya kare kansa daga zargin da ake yi masa da ba da umarni ga jami'an tsaro wajen kashe ɗarurruwan jama'a a shekarun 2011.

https://p.dw.com/p/1CtbG
ARCHIVBILD Hosni Mubarak
Hoto: picture-alliance/AP Photo

Wata kotu a Masar ta ce nan gaba a ranar 27 ga watan da ke kamawa za ta bayyana hukunci da ta zartas a kan tuhumar da ake yi wa tsohon shugaban ƙasar Hosni Mubarak, da laifin ba da umarnin aikata kisa a kan masu yin borai na neman sauyi wanda ya kai ga share gwamnatinsa a shekarun 2011.

A lokacin da yake ammsa tambayoyi a wani zaman da kotun ta yi, Mubarak ya musunta zargin ba da umarnin ga wasu manyan jami'an tsaro wajen kashe masu zanga- zangar. Sannan ya ce wannan watakila ita ce bayanasa ta ƙarshe, saboda yadda ya ce rayuwarsa take kusan ƙarshe.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu