1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar CENI a Chadi ta ɗage ranar zaɓe

Sadissou YahouzaSeptember 27, 2010

Hukumar zaɓen a ƙasar Chadi ta bayyana saban jaddawalin zaɓɓuɓukan da za a shirya shekara mai zuwa.

https://p.dw.com/p/PNim
Shugaban ƙasar Chadi Idriss Deby ItnoHoto: AP

Hukumar zaɓen ƙasar Chadi  ta ɗage zaɓukan shugaban ƙasa,na majalisar dokoki da ƙananan hukumomin zuwa shekarar 2011 sakamakon matsalolin shirye-shirye.

Hukumar zaɓen ta bayyana cewa a saban jaddawalin zaɓen, za a gudanar da zaɓen majalisar dokoki a ranar 20 ga watar Febrairu, na ƙananan hukumomi kuma 27 ga watan Maris kana a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa zagaye na farko a ran takwas ga watan Mayun 2011.

Jaddawalin farko ya tanadi shirya zaɓɓuɓkan ´yan majalisa da na ƙananan hukumomi kamin ƙarshen shekara da mu ke ciki.

Baki ɗaya, mutane miliyan huɗu da rabi ne, ya cencenta su kaɗa ƙuri´a a wannan zaɓɓuɓuka.

Mawallafi: Pinaɗo Abdu

Edita: Yahouza Sadissou Madobi