1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar zaɓe a Madagaska ta tsaida ranar zaɓe

August 23, 2013

Za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a ranar 25 ga watan Oktoba da ke tafe, kana ta ce ce a yi zaɓen 'yan majalisun dokoki a rana 20 ga watan Disamba.

https://p.dw.com/p/19Uz5
Madagaskars langer Weg zur Wahl Aufgenommen von Friederike Müller am 19.08.2013 in Antananarivo, Madagaskar. Zulieferer: Friederike Müller. Bild 4: Die Entscheidung des Spezialgerichtshofes ist Thema Nummer eins in Madagaskar Aufgenommen von Friederike Müller am 19.08.2013 in Antananarivo, Madagaskar
Hoto: Friederike Müller

Wannan shi ne karo na uku kennan da hukumar ke ɗage zaɓen wanda a wannan jiƙon ta ce, ta yi hakan ne domin ta kawo gyara ga rejistar 'yan takarar guda uku da ta soke waɗanda za su tsaya a zaɓen shugaban ƙasar.

Waɗanda suka haɗa da Andry Rajoelina shugaban wucin gadin, da uwargidan tsohon shugaban ƙasar Marc Ravalomanana da kuma tsohon shugaban ƙasar Didier Ratsiraka. Wanan zaɓe dai zai kwo ƙarshen rikicin siyasar da aka kwashe kusan shekaru fuɗu da rabi ana yi a ƙasar tun bayan faɗuwar gwamnatin Marc Ravalomanana a shekarun 2009.

Mawalllafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman