1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumomin Kenya na gudanar da bincike

Charlotte Chelsom-PillSeptember 25, 2013

Ministan cikin gida na ƙasar ya ce ƙasashen duniya waɗanda suka haɗa da Ingila da Amirka da Isra'ila da Jamus da kuma Canada na taimaka musu wajen gudanar da bincike.

https://p.dw.com/p/19oah
Kenya Defence Forces soldiers take their position at the Westgate shopping centre, on the fourth day since militants stormed into the mall, in Nairobi September 24, 2013. Somalia's al Shabaab Islamist group said on Tuesday there were "countless dead bodies" in the Westgate shopping centre as security forces searched for militants still holed up in the complex after a weekend attack that authorities say killed 62 people. REUTERS/Noor Khamis (KENYA - Tags: CIVIL UNREST CRIME LAW MILITARY)
Hoto: Reuters

jami'an na yin binciken ne domin gano sauran gawarwaki da sauran bama-bamai watakila, waɗanda basu tashi ba a cikin kanti nan na Westgate wanda 'yan ƙungiyar Al-Shabaab suka kai hari a kansa tun ran Asabar.

Ministan josephe Ole Lenku ya ce za a ɗauki lokaci ana gudanar da aikin na bincike kusan mako guda. Gwamnatin ta Kenya ta ayyana zaman makoki na kwanaki uku domin yin alhini na asarar rayukan da aka samu na mutane 61 kana sama da ɗari biyu suka jikkata. Ƙungiyar ta Al-Shabaab a kan shafinta na Twitter ta ce mutane 137 suka mutu.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh