1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukuncin kisa ga membobin Boko Haram a Chadi

Salissou BoukariAugust 28, 2015

Kotun da ke sauraron manyan laifuka a kasar Chadi, ta yanke wa wasu mutane 10 da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne hukuncin kisa, bayan kamasu da laifi.

https://p.dw.com/p/1GNct
Hoto: Reuters/M. Ngarmbassa

Wannan shari'a da ta gudana a wannan Jumma'a ta tabbar da hukuncin kisa ga duk mutanen goma, sannan kuma kotun ta ce makaman da aka kama za a mika su ga hannun gwamnatin kasar ta Chadi. Sannan wasu kayayyaki na razanar da al'umma, su kuma za a lalatasu. Wannan dai shi ne karo na farko da aka gudanar da wata shari'a kan wasu da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne a kasar ta Chadi. Mutanen goma dai, an kama su ne da laifin shirya kai hare-haren kunar bakin wake da suka yi sanadiyar rasuwar mutane da dama a watan Juni a birnin na Ndjamena fadar gwamnatin kasar.