Hukuncin kisa ga membobin Boko Haram a Chadi
August 28, 2015Talla
Wannan shari'a da ta gudana a wannan Jumma'a ta tabbar da hukuncin kisa ga duk mutanen goma, sannan kuma kotun ta ce makaman da aka kama za a mika su ga hannun gwamnatin kasar ta Chadi. Sannan wasu kayayyaki na razanar da al'umma, su kuma za a lalatasu. Wannan dai shi ne karo na farko da aka gudanar da wata shari'a kan wasu da ake zargin 'yan kungiyar Boko Haram ne a kasar ta Chadi. Mutanen goma dai, an kama su ne da laifin shirya kai hare-haren kunar bakin wake da suka yi sanadiyar rasuwar mutane da dama a watan Juni a birnin na Ndjamena fadar gwamnatin kasar.