1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukuncin kotu kan rikicin jam'iyyar MNSD

Maman Kanta/Gazali Abdu TasawaJuly 23, 2015

Kotu ta dage takunkumin da ya haramtawa bangaren Albade Abuba yin magana da sunan jam'iyyar MNSD Nasara a cikin rikicin da ya hada bangaran Albaden da na shugaban jam'iyyar na kasa Alhaji Seini Umaru

https://p.dw.com/p/1G3OJ
Seini Umaru shugaban jam'iyyar MNSD Nasara
Hoto: MNSD

A jamhuriyar Nijar kotun daukaka kara wato Cour d'Appel ta birnin Yamai ta karya matakin da ya haramtawa bangaran Albade Abuba tsohon magatakardan jam'iyyar MNSD Nasara yin magana da sunan jam'iyyar. Kotun ta bayyana haka ne lokacin wani zama da ta gudanar a wannan Laraba.Tuni dai Bangaran Albade Abuban ya bayyana gamsuwarsa da wannan hukunci .

Sai dai rikicin shari'ar jam'iyar MNSD Nasara dake adawa,tsakanin shugaban jam'iyar na kasa Alhaji Seini Umaru,da bangaren Albade Abuba bai kare ba,inda yanzu haka suke jiran sakamakon wata shari'ar a kan wani karan da bangaren Alhaji Seini Umaru din ya shigar a gaban kotun koli mai hurumin karya shari'a wato Cour de Cassation.

Albade Abouba abokin hamayyar Seini Umaru shugaban MNSD Nasara
Hoto: DW/M.Kanta

Rikicin Jam'iyyar ta MNSD Nasara madugar jam'iyyun adawar kasar ya samo tushe ne tun a lokacin kafa gwamnatin hadin kan kasa inda bangaren Albade Abuba ya karbi tayin shiga gwmnati a yayinda bangaren Seini Umaru ya kauracewa tayin a bisa hujjar cewa ya sabawa doka.