1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hulda za ta gyartu tsakanin EU da Turkiyya

Abdullahi Tanko BalaSeptember 9, 2016

Turkiyya da Kungiyar tarayyar Turai sun amince a yau Juma'a su sassauta sabanin da ke neman haifar da nakasu ga yunkurin karbar Turkiyyar a kungiyar tarayyar Turai:

https://p.dw.com/p/1JzIx
EU Türkei Mogherini und Hahn in Ankara
Hoto: picture-alliance/AA/F. Aktas

Babbar Jami'ar harkokin waje ta kungiyar tarayyar Turai Federica Mogherini da kwamishina mai kula da fadada wakilci a kungiyar tarayyar Turai Johannes Hahn wadanda ke wata muhimmiyar ziyara ta kololuwa a Turkiyyar sun ce za'a bude sabon babi kan shirin karbar kasar a Kungiyar ta EU yayin da batun sassaucin Visa kuma za'a ci gaba da tattaunashi. A baya-bayan nan manyan jami'ai na Turkiyya da kungiyar tarayyar Turai sun yi ta cacakar baka bayan yunkurin juyin mulkin inda Hedikwatar tarayyar Turai a Brussels ta yi kakkausar suka kan tsauraran matakan da Turkiyya ta dauka yayin da fadar gwamnatin a Ankara kuma ta soki tarayyar turai da rashin nuna goyon baya.