1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hunkunci a kan wasu 'yan sanda a Masar

Abdourahamane HassaneMarch 4, 2015

Kotun ɗaukaka ƙara a ƙasar Masar ta tabbatar da hukuncin ɗaurin shekaru goma na zaman gidan yari ga wasu 'yan sanda guda biyu.

https://p.dw.com/p/1El8r
Ägypten Proteste zum Jahrestag des Aufstands in Kairo 25.01.2015
Masu zanga-zanga a MasarHoto: Reuters/M. Abd El Ghany

Kotun ta samu 'yan sandan da laifin kashe wani mai fafutuka mai yin rubuce-rubuce ta shafin Intanet na Blogs wato Khaled Said a shekarun 2010.

Mutumin da ake kallon a matsayin jigo wajen ƙaddamar da juyin juya halin da ya share gwamnatin Hosni Mubarak daga mulki a shekaru 2011.