1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hunkunci a kan 'yan Taliban

Abdourahamane HassaneApril 30, 2015

Wata kotu a Pakistan ta yanke hukuncin ɗaurin rai da rai ga wasu mutane guda goma wanda suka harbi Malala.

https://p.dw.com/p/1FIIc
Friedensnobelpreis 2014 Malala Yousafzai,
Hoto: Reuters/Darren Staples

Kotun wacce ke yaƙi da ta'addanci ta samu mutanen da laifin yunƙurin hallaka Malala a shekaru 2012 a lokacin tana da shekaru 15.

A harin da suka kai mata a kan hanyarta ta zuwa makaranta a maifarta a garin Mingora da ke a yankin arewa maso yammacin Pakistan inda suka harbeta a ka.Harin wanda Ƙungiyar Taliban ta yi iƙirarin kai wa a cikin wata wasiƙa da ta aike wa Malala ta ce ta yi haka ne a kan fafutukar da take na samar da ilimin boko ga yara a Pakistan.