1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

ICC: Soma shari'ar rosa kaburburan waliyai a Mali

Gazali Abdou TasawaSeptember 30, 2015

A wannan Laraba ce Ahmad Al-Faqi Al-Mahdi jagoran wata kungiyar masu kaifin kishin Islama ta kasar Mali ke fiskantar shari'a bisa umarnin rusa wuraren tarihi a Tombouctou

https://p.dw.com/p/1Gfp9
Mali Timbuktu Weltkulturerbe Zerstörung AKTUELLES BILD
Hoto: Getty Images

Jagoran kungiyar masu kaifin kishin Islama ta kasar Mali da ke da alaka da kungiyar Al-kaida, zai bayyana a gaban kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya wato ICC. Kotun na zargin mutuman mai suna Ahmad Al-Faqi Al-Mahdi da bada umarnin rusa kaburburan waliyai na tarihi a shekara ta 2012.

Wannan dai shi ne karo na farko da kotun ta ICC za ta gudanar da shari'a kan batun rusa wasu wuraren tarihi na addini. A karshen makon da ya gabata ne dai aka kawo Ahmad Al-Faki Al-Mahdi wanda ke tsare a kasar Nijar zuwa gidan kurkukun kotun ta ICC da ke a birnin Hague.