1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Binciken ICC a Falasdinu kan aikata laifukan yaki

January 16, 2015

Kotun hukunta masu aikata manyan laifuka ta kasa da kasa ICC ta ce ta bude babin farko na bincike kan aikata laifukan yaki a Falasdinu.

https://p.dw.com/p/1ELvJ
Hoto: imago/Eibner Europa

Wannan dai shi ne matakin farko a hukumance da aka dauka wanda ka iya kaiwa ga tuhumar Isra'ila kan aikata laifukan yaki a Falasdinun. Babbar mai gabatar da kara a kotun ta ICC Fatou Bensouda ta bayyana cewa za ta gudanar da bincike a matakin farko mai cikakken 'yanci wanda ba nuna banbanci a ciki. A ranar daya ga wannan wata na Janairu da muke ciki ne dai mahukuntan Falasdinun suka bukaci kotun da ta gudanar da bincike kan abubuwan da Isra'ila ta aikata a yankin Zirin Gaza tun daga watan Yunin shekarar da ta gabata ta 2014, kafin washe gari su mika bukatarsu na zamowa mamba a kotun ta ICC.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Mohammad Nasiru Awal