1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

IMF ta nemi karin tallafi ga Girka

November 15, 2012

Hukumar IMF ta nemi kasashen Turai, su tallafa wajen rage yawan bashin kasar Girka.

https://p.dw.com/p/16kA8
Hoto: SAKIS MITROLIDIS/AFP/Getty Images

Hukumar ba da lamuni ta duniya, IMF, a wannan Alhamis ta nemi ƙasashen Turai su saka hannu wajen rage bashin ƙasar Girka, inda hukumar ta ce, ta daina bada gudumawar ceto tattalin arzikin ƙasar ta Girka.

Hukumar ta ƙara lokacin da Girka za ta biya bashi zuwa shekaru huɗu. Amma hukumar ta IMF, ba ta bayyana dalla-dalla yadda ta ke bukatar ƙasashen za su tallafa wa Girka ba.

Shugaban hukumar ta IMF, Christine Lagarde za ta katse ziyarar kasashen Asiya, domin halartar taron ministocin kudin kasashen masu amfani da kudin Euro, bisa ruikicin na kasar ta Girka, ranar Talata mai zuwa.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Mohammad Nasir Awal