1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukuncin kisa kan wani Malami a Indonesiya

Salissou Boukari
June 22, 2018

Wata kotu a birnin Jakarta na kasar Indonesiya ta yankewa wani Malami mai tsatsauran ra'ayin adinin Musluncin hukuncin kisa a wannan Juma'a, bayan da aka same shi da laifin bada izinin kai wasu jerin hare-hare.

https://p.dw.com/p/303dh
Indonesien einer der Angeklagten Homosexuellen im Gerichtssaal in Banda Aceh
Hoto: Reuters

A kasar a shekara ta 2016 ne dai wannan Malami mai suna Aman Addurrahman ya bada izinin kai wani hari a kasar ta Indonesiya, wanda ke a matsayin hari na faro da kungiyar IS ta dauki alhakin kai wa a wannan kasa da ke yankin Kudu maso gabashin Asiya.

Kotun dai ta samu babban malamin mai wa'azi a kasar mai suna Aman Addurrahman da laifin kitsa hare-haren da aka kai a kasar da suka yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu, wanda a cikinsa maharan guda hudu suka mutu.

Shugaban kotun mai suna Akhmad Zaini, ya kara da cewa an sami wannan malamin kuma da hannu cikin wasu hare-hare da aka kai a kasar. Sai dai Malamin da ke zaune ya yin yanke masa hukuncin bai nuna wani yanayi na nadama ba.