1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

INEC ta yi wa Jam'iyyar APC regista

July 31, 2013

Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya watau INEC, ta amince da yiwa jam'iyyar adawa ta APC regista, wadda za ta kalubalanci jam'iyyar PDP a zabukan 2015.

https://p.dw.com/p/19HnL
Attahiru Jega, Independent National Electoral Commission Chairman, declares Nigeria's incumbent President Goodluck Jonathan as the winner of last Saturday's presidential election, in Abuja, Nigeria, Monday, April 18, 2011. Jonathan clinched the oil-rich country's presidential election Monday, as rioting by opposition protesters in the Muslim north highlighted the religious and ethnic differences still dividing Africa's most populous nation. (Foto:Sunday Alamba/AP/dapd)
Hoto: AP

Bayan kwashe lokaci tana jan kafa, hukumar zabe mai zaman kanta ta INEC a Najeriya, ta sanar da yi wa jam'iyyar hadaka ta 'yan adawa ta APC regista. APC dai ta kunshi manyan jam'iyyun adawan Najeriya guda uku, wadda ake ganin za ta kasance babbar kalubale ga Shugaba Goodluck Jonathan da jam'iyyarsa ta PDP a zabukan da za su gudana a 2015, idan Allah ya kaimu.

Jami'in yada labaru na hukumar zaben Najeriyar Mr Nick Dazan ya bayyana cewar, sun dauki wanan mataki ne bayan da jamiyyar ta APC ta cika dukkanin kaidojin da hukumar zaben ta gindaya ga duk wata jam'iyya kafin ta kai ga samun rijista a cikin kasar.

Har zuwa yanzu dai Kungiyar African Peoples Congress na gaban kotu domin kalubalantar cewa ita ce ta fara gabatar da bukatar ayi mata rijista da wannan suna na APC a matsayin jamiyyar siyasa a Najeriyar.

Jam'iyyar adawa ta APC dai ta kunshi manyan 'yan siyasa daga arewa kamar Janar Mohammdu Buhari mai ritaya, da kuma irinsu tsohon gwamnan jihar Lagos Ahmed Bola Tinubu daga yankin kudancin Najeriya.

Mawallafi: Uwais Abubakar Idris
Edita : Zainab Mohammed Abubakar