1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iraki: An kashe mutane 20 a kasuwa

Abdul-raheem Hassan
November 21, 2017

Mutane 20 sun mutu, a wani harin bam da dan kunar bakin wake ya kai a cikin babbar mota a kusa da kasuwar garin Tuz Khurmatu da ke kudancin birnin Kirkuk.

https://p.dw.com/p/2o0A1
Irak Kämpfe um Mossul
Hoto: picture-alliance/AP Photo/F. Dana

Jami'an 'yan sanda da likitoci a asibitocin da ke arewacin Iraki sun tabatar da jikkatar fararen 40, inda ake fargabar adadin mutuwar ka iya karuwa sakamakon mumunan raunuka da harin yahaddasa.

Ma'akatar cikin gida a kasar Irak, sun yi Allah wadai da wannan mumunar harin. Babu kungiyar da ta dau alhakin wannan harin, amma yankin ya sha fuskantar zafafan hare-haren kungiyar I S.Sojoji sun gama da kungiyar I S a Iraki