1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iraki za ta bawa Kurdawa kariya

Abdul-raheem Hassan
September 30, 2017

Firaiministan Iraki Haider al-Abadi ya bayyana kudurin gwamnatin Iraki, na kare yankin Kurdawa daga dukkanin wasu hare-hare da za su iya fuskanta daga kasashen da ke adawa da yunkurin neman ballewa.

https://p.dw.com/p/2l210
Haider Abadi
Firaiministan Iraki, Haidar al-AbadiHoto: AFP/Getty Images

Haidar al-Abadi ya wallafa a shafinsa na twitter cewa " Za mu kare 'yan uwanmu Kurdawa kamar yadda muke bawa saurarn fararen hula a Iraki kariya, ba za mu taba bari a ci mutuncin 'yan uwanmu ko ta wane hanya ba, ba za mu zuba idanu muna kallo a kawo musu hari ba mu karesu ba."

To sai dai wannan ikirari na Firaiministan na zuwa ne a dai-dai lokacinda gwamnatin Iraki, ta kaddamar da girke rundunar sojin hadin gwiwa da Turkiyya a kan iyakar kasar.

Yankin Kurdawan dai na ci gaba da fuskantar wariya tun bayan da suka jefa kuri'ar raba gardama da neman 'yanci a ranar Litinin da ta gabata. A yanzu dai kasashe da ke makota irin su Iran da Turkiyya na cikin kasashen da suka dauki matakan katse huldar kasuwanci da zirga-zirgan jiragen sama a yankin kurdawan.