1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Neman sakin shugaban 'yan Shi'a a Najeriya

Yusuf BalaDecember 18, 2015

Masu fafutikar kare hakkin bil Adama dai na cewa mutanen da suka rasu sakamakon rikicin sun kai mutum dubu daya.

https://p.dw.com/p/1HQ9I
Iran Protest
Al'ummar Iran na zanga-zangaHoto: Tsanim

Dubban al'ummar kasar Iran mabiya tafarkin Shi'a sun gudanar da zanga-zanga a titunan birnin Teharan a wani bangaren na nuna takaicinsu a kisan da aka yi wa daruruwan 'yan uwansu a wannan tafarki da ke a Najeriya.

Daruruwan 'yan Shi'a ne dai ake sa ran sun halaka bayan wata taho mu gama da jami'an tsaro a ranar Asabar da ta gabata a Najeriya. Shi dai shugaban mabiya wannan tafarki na Shi'a malam Ibrahim el-Zakzaky ya samu raunika sakamakon harbin bindiga a lokacin wannan taho mu gama da jami'an soji na kasar.

Masu fafutikar kare hakkin bil Adama dai na cewa mutanen da suka rasu sakamakon rikicin sun kai mutum dubu daya. Su dai masu zanga-zangar na birnin Tehran sun bukaci sakin malam Zakzaky ba tare da gindaya wasu sharuda ba.