Isra´ila ta kai hari a Gaza
June 27, 2007Wannan shine hari na farko mafi muni, da dakarun bani yahudu su ka abkawa Gaza, tun bayan da ƙungiyar Hamas ta mamaye wannan ziri.
A cewar opishin ministan tsaron Isra´ila, wannan hari na matsayin martani, ga rokokin da wasu yan takifen Hamas su ka cillawa Isra´ila.
Shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas ya Allah wadai da wannan hari, wanda a cewar sa zai kara maida hannu agogon baya, a yunƙurin cimma zaman lahia, tsakanin Isra´ila da Palestinu.
A ɓangaren diplomatia shugaban hukumar Palestinawa na ci gaba da samun goyan baya, a dangane da tawayen ƙungiyar Hamas.
A ɗaya wajen kuma, Mahamud Abbas ya tsige shugaban rundunar tsaron fadar sa, wanda ya tuhuma da rashin sanin makamar aiki, a sakamakon kashin da dakarun sa su ka sha, daga ƙungiyar Hamas a zirin Gaza.