1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Isra'ila ta kai hari Gaza

February 18, 2018

Jiragen yakin Isra'ila sun kai hare-hare kan yankin zirin Gaza, bayan raunin da wasu sojojin kasar suka ji sakamakon tashin bom jiya Asabar a yankin Falasdinawa.

https://p.dw.com/p/2ssn3
Palästina Ausschreitungen in Gaza
Hoto: Reuters/I. Abu Mustafa

Jiragen yakin Isra'ila sun kai hare-hare kan yankin zirin Gaza, bayan raunin da wasu sojojin kasar suka ji sakamakon tashin bom a ranar Asabar a yankin Falasdinawa. Ma'aikatar tsaron Isra'ilar ta ce ta afka wa akalla sansanonin shida da ke yankin na Falasdinawa, saboda amannar da suka cewar falasdinawan sun dasa boma-boman da gangan a Juma'ar da ta gabata, kuma suka ajiye tutarsu.

Kamfanin dillancin labaran Falsdinu Wafa, ya ce wasu makamai masu linzami da Isra'aila ta harba, sun lalata gidaje a wurare uku a Gaza. Lamura dai sun kara tabarbarewa tsakanin Isra'ila da Falasdinu ne tun cikin watan Disamba, lokacin da Shugaban Amirka Donald Trump ya bayyana amincewa da birnin Kudus a matsayin fadar gwamnatin Isra'ila.