1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Issac Yacouba Zida ya zama shugaban Burkina Faso

Salissou BoukariNovember 1, 2014

Rundunar sojan Burkina Faso ta zabi Kanar Issac Yacouba Zida a matsayin jagoran gwamnatin rikon kwarya, a wata sanarwar da ta gabatar dazu-dazun nan.

https://p.dw.com/p/1DfWD
Burkina Faso - Oberst Isaac Zida
Hoto: ISSOUF SANOGO/AFP/Getty Images

Sojojin kasar Burkina Faso sun amince da zaben Laftanan Kanar Isaac Yacouba Zida a matsayin sabon shugaban kasar da zai jagoranci wannan kasa na rikon kwarya, bayan murabus din da shugaba Blaise Campaore yayi, wanda yanzu haka yake gudun hijira a birnin Yamouskro na kasar Cote d'Ivoir. A wata sanarwa da rundunar sojan kasar ta Burkina faso ta fitar a dazu-dazun nan bayan kammala wani zaman taro na manyan sojojin kasar a birnin Wagadugu, sun tabbatar cewa ga baki dayan su sun amince da Kanar Issac Zida a matsayin sabon shugaban kasar na rikon kwarya, inda babban hafsan hafsoshin kasar Janar Nabere Honore Traore ne ya sa hannu ga sanarwar.