1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

An kama hanyar sulhunta rikicin maye gurbin Merkel

Abdoulaye Mamane Amadou
April 11, 2021

Bangarorin da ke takaddama kan maye gurbin shugabar gwamnatin Jamus na ci gaba da jayayya kan tantance wanda zai tsaya takara da sunan kawancen masu mulki.

https://p.dw.com/p/3rqAc
Bildkombo Laschet Merkel Söder

Mutanen nan biyu da ake hasashen daya zai maye gurbin shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel wato Armin Lasche na jam'iyyar CDU da Markus Söder na CSU za su yi wata ganawar sirri a yau Lahadi, da kusoshin kawancen jam'iyyun na CDU da CSU masu mulkin Jamus a birnin Berlin.

Ana dai fama da tababa kan wanda zai maye gurbin shugbar gwamnati da ke shirin bankwana da mulki a wannan shekara, tsakanin Armin Laschet da yanzu hakan ke jagorancin jamiyyar CDU ta Misis Merkel da abokin hamayyarsa Markus Söder na jam'iyyar CSU mai kawance da ita.

Bangarorin biyu dai za su tattauna ne kan batun sabonta tarayyar Jamus nan da gaba, to amma sai da dama na ganin da akwai rarrabuwar kawuna kan tantance mutanen biyu, duk da yake Markus Söder na kara samun kwarjini da goyon bayan 'yan majalisar dokoki daga kawancen masu mulkin.