1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jama'a na cikin wahala a yanki arewacin Mali

November 8, 2012

Ƙungiyar agaji ta Red Cross ta ce rashin tsaro da ake fama da shi a arewacin Mali haɗe da ƙarancin cimmaka ya saka wasu jama'ar dubu 500, cikin wani hali na rashin tabbas

https://p.dw.com/p/16fn3
Militiaman from the Ansar Dine Islamic group, who said they come from Niger and Mauritania, ride on a vehicle at Kidal in northeastern Mali in this June 16, 2012 file photograph. To match Special Report MALI-CRISIS/CRIME REUTERS/Adama Diarra/Files (MALI - Tags: CIVIL UNREST CRIME LAW POLITICS)
Ansar Dine Kämpfer in MaliHoto: REUTERS

Shugaban ƙungiyar Peter Maurer ya ce tun bayan da ƙasar ta rabu gida biyu a cikin watan Maris da ya gabata ;ayyukan jin ƙaI da suke yi, suka ja da baya ,saboda wahalolin da suke gamuwa da su a yankin na arewaci.

Ya ce mutanen,na buƙatar agaji saboda su ka ɗai karan kansu, ba zasu iya ɗaukar nauyin ɗawainiyar su ba.Nan gaba ne kuma a ranar lahadi mai zuwa aka shirya shugabannin ƙungiyar ƙasashen yammancin Afirka na ECOWAS ,zasu gudanar da wani taro a birnin Abuja na Tarrayar Najeriya domin tantance matakai na ƙarshe a kan yan tawayen na Mali gabannin samun izinin fara kai harin daga MDD.

A ranar talata da ta gabata ne ,man'yan kwamandojin yaƙi na ƙungiyar ƙasashen yammancin Afirka wato ECOWAS ko kuma CEDEAO;suka amince da wani tsari na sake ƙwato yankin arewacin ƙasar Mali ,wanda ke cikin hannu ƙungiyoyin yan tawayen tun watanni takwas da suka wuce .

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu