1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jama'a sun kauracewa rumfunan zaben Masar

Usman Shehu UsmanNovember 22, 2015

Rukuni na biyu a zaben majalisar dokoki ya gudana amma 'yan kalilan suka fito, duk kuwa da baza jami'an tsaro a fadin kasar don gudun barkewar tarzuma

https://p.dw.com/p/1HAR0
Ägypten Wahlen Wahllokal in Kairo Wahlurne
Hoto: Reuters

A kasar Masar wannan Lahdi 22.11.2015 aka gudanar da zaben rukuni na biyu na 'yan majalisar dokoki, domin samar da majalisar da za ta yi wa kasar doka. Sai dai a cewar masu aiko da rahotanni zaben rukunin na biyun kamar rukunin farko da aka yi, kusan 'yan kalilan mutane aka gani a rumfuna, bayan da mutanen suka kauracewa fita zabe. Dama dai tun a shekara ta 2012, sojoji suka rusa majalisar dokoki ta farko da jama'a suka zaba bisa tsarin demokradiya, bayan da suka shigar da kara a kotu. Duk da cewa rumfunan sun kasance wayam amma an baza tarin sojoji don gadin 'yan rumfunan zabe, ganin irin tarzuma da kasar ke fiskanta.