1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamiyyar Kadima ta Sharom taja daga

January 16, 2006
https://p.dw.com/p/BvC1

Sabuwar Jamiyyar Mr Sharon, wato Kadima ta nada Mr Ehud Olmert a matsayin shugabanta na riko da zai jagorance ta a lokacin zaben gama garri da aka shirya yi a ranar 28 ga watan maris na wannan shekara da muke ciki.

A cewar wata sanarwa data fito daga jamiyyar ta Kadima, ta tabbatar da cewa daukar wannan mataki ya biyo bayan irin halin da yake ciki ne a yanzu na matsananciyar rashin lafiya.

Idan dai an tuna Faraminista Ariel Sharon ya tsinci kann sa ne a cikin wannan hali bayan ya fuskanci mummunan bugun zujiya, data haifar masa da tiyata a cikin kwakwalwarsa.

Ya zuwa yanzu dai bayanai sun nunar da cewa har yanzu Mr Sharon na cikin dogon hali na suma, wanda likitoci suce ci gaba da kasancewa a wannan hali hatsari ne ga rayuwar faraministan.