1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus da Faransa sun ce a mutunta yarjejeiyar Ukraine

August 28, 2017

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel da shugaba Emmanuel Macron na kasar Faransa, sun yi kira ga kasar Rasha da ta kara kaimin ganin yarjejeniyar tsakaiga wuta a gabashin kasar Ukraine ta tabbata.

https://p.dw.com/p/2izWo
G20-Gipfel Gespräch  Merkel Putin Macron
Hoto: picture alliance/dpa/T. Schwarz

Shugabannin biyu sun ce suna matukar damuwa da halin tabarbrewar da al'amura ke yi a gabashin na Ukraine, a saboda haka ne suke bada hankali kan lamarin da ke faruwa. Sun gana ta waya kai tsaye da shugaba Putin na Rasha da ma Petro Poroshenko na kasar Ukraine dangane da matsalar. Yarjejeniyar da jagororin manyan kasashen biyu ke batu a kanta dai, yarjejeniya ce da aka sanya wa hannu a shekara ta 2015 a garin Minsk, babban birnin kasar Belarus. Akalla dai mutane dubu 10 ne suka salwanta a yakin da ake kafsawa a gabashin kasar ta Ukraine.