1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus da Turkiyya an sasanta

February 17, 2018

Gwamnatocin Jamus da Turkiyya sun amince da bayar da himma ga harkokin bunkasa kasashen biyu bayan takaddamar da ta wakana tsakaninsu mai nasaba da tsare wani dan jarida a Turkiyya a bara.

https://p.dw.com/p/2sqPv
54. Münchner Sicherheitskonferenz MSC - Sigmar Gabriel und Mevlüt Cavusoglu
Sigmar Gabriel tare da Mevlut Cavsoglu na TurkiyyaHoto: picture alliance/dpa/S. Hoppe

Ministocin harkokin wajen kasashen Jamus da Turkiyya, sun bayyana aniyar kyautata hulda tsakanin kasashen biyu ta fannonin tsaro da kuma tattalin arziki, bayan sakin dan jaridan nan Bajamushe mai asali da Turkiyya Denis Yücel a jiya Juma'a. A cewar Mevlut Cavusoglu wanda shi ne ministan harkokin wajen Turkiyya, manyan kasashen biyu, sun shawo kan daya daga cikin takaddamar da ke tsakaninsu, don haka ba tare da wata-wata ba, kamata ya yi su koma ga harkokin da za su kai su gaba.

Shi ma a nashi bangaren ministan harkokin wajen Jamus Sigma Gabriel, cewa ya yi ba laifi bane a sami sabanin ra'ayi tsakanin Jamus da Turkiyya, sai dai kuma lallai ne a martaba juna saboda makomar kasashen biyu. Zaman jarum na shekara guda dan jarida Deniz Yücel ya yi a Turkiyyar bisa zargin ta'addanci dai ya tsananta huldar diflomasiyya tsakanin Jamus din da kuma makwabciyarta wato Turkiyyar.