1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jonathan ya ki yi wa 'yan Boko Haram afuwa

March 7, 2013

Shugaban Tarayyar Najeriya Goodluck Ebele Jonathan ya ya da zango a jihar Yobe kafin ya wuce zuwa Borno. Sai dai ya ki amsa kirar da masu ruwa da tsaki na jihohin biyu suka yi masa na yi wa 'yayan Boko Haram afuwa.

https://p.dw.com/p/17tC3
Hoto: picture alliance / dpa

Daga saukar Shugaban a garin Damaturu inda aka tsaurara matakan tsaro tare da takaita zirga-zirgar mutane a cikin sa, ya fara kai caffar ban girma ga Sarkin Damaturu Ba Shehu Umar Ali Ibn El-Kenemi. Daga nan ne kuma shi da tawagar sa suka wuce fadar gwamnatin inda ya gana da masu ruwa da tsaki a jihar tare da jin korafe-korafen su ciki kuwa har da na tsohon gwamnan jihar Senata Bukar Abba Ibrahim.

Dukkanin alamu dai sun nuna cewa babu wani rubutaccen sako da shugaban ya je da shi garin don gabatarwa al'umma.Maimakon haka ma dai ya mai da jawabi tare da kare gwamnatin sa game da irin korafe-korafen da al'umma suke yi dangane da yadda gwamnatin sa tayi watsi da yankin da rikici da gurgunta. Dangane da bukatar da aka gabatar na neman yi wa ‘yan kungiyar Jama'atu Ahlussunah Lidda'awati wal jihad da aka fi sani Boko Haram Afuwa, Jonathan ya ce ba za ta yiwu ba.

Goodluck Jonathan Nigeria, Kano Bombenanschlag
Jonathan na kai ziyarar ban girma a fada a lokacin da ya kai ziyara wata jihaHoto: picture-alliance/dpa

"Ba'a yin Afuwa ga wadanda ke ayyukan su a boye, ‘yan Boko Haram suna aikace-aikacen su ne a boye don ba wanda zai fito ya bayyana kan sa cewa shi dan Boko Haram ne ,sabanin yadda aka yi a yankin Niger-Delta inda in ka nemi Shugabannin za su zo ku zauna da su. Saboda haka babu maganar yin Afuwa a yanzu ga ‘yan Boko Haram."

Yadda al'uma suka dauki matakin Jonathan

Wannan sako bai yi wa da dama daga cikin mahalarta wannan taro dadi ba kamar yadda fuskokin su ya nuna ganin a baya sun yi fatan shugaban zai yi amfani da wannan dama na ziyarar ta sa wajen sanar da shirin yin Afuwa ga masu gwagwarmaya da makaman. Da yawa daga cikin al'ummar jihar Yobe ba su yi marhabin da wannan ziyara ba musamman ganin babu wani sako na musamman da shugaban ya je da shi, ga kuma mummunar takurawa da suka ce an musu ta hana fita ko don neman na sawa a bakin Salati.

A picture taken on April 18, 2011 shows Nigerian police enforcing a curfew in the capital of Bauchi state, nothern Nigeria, after riots, run by muslim youth, broke out in Bauchi. Nigeria's Goodluck Jonathan has been declared winner of presidential elections in a landmark vote that exposed regional tensions and led to deadly rioting in the mainly Muslim north. Jonathan, the incumbent and first president from the southern oil-producing Niger Delta region, won 57 percent of the vote in Africa's most populous nation, easily beating his northern rival, ex-military ruler Muhammadu Buhari. AFP PHOTO / Tony KARUMBA (Photo credit should read TONY KARUMBA/AFP/Getty Images)
An tsaurara matakn tsaro a Yobe da Borno sakamakon ziyarar Jonathan a jihohinHoto: Getty Images/AFP

Wannan ziyara ta shugaban Jonathan dai wacce aka ka watsa kai tsaye a gidan talabijin na kasar ta sha suka daga bangarorin al'ummar yankin, ganin irin jinkirin da aka samu na tsawon shekara hudu ana rikici a yankin amma bai taba takowa ko kuma yin jaje bare aikewa da gudumawa ba.

Rahoto cikin sauti na kasa

Mawallafi: Al-Amin Suleiman Mohammad
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe