1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Juyin mulki a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

March 24, 2013

'Yan tawayen Seleka sun kifar da shugaba François Bozize daga karagar mulki,kuma sun yi alkawarin shirya zabe cikin gaggawa.

https://p.dw.com/p/183QN
Central African Republic President Francois Bozize (centre L, in blue) speaks to a crowd of supporters and anti-rebel protesters during an appeal for help, in Bangui December 27, 2012. Bozize on Thursday appealed for France and the United States to help push back rebels threatening his government and the capital, but Paris said its troops were only ready to protect French nationals. The exchanges came as regional African leaders tried to broker a ceasefire deal and as rebels said they had temporarily halted their advance on Bangui, the capital, to allow talks to take place. Picture taken December 27, 2012. REUTERS/Stringer (CENTRAL AFRICAN REPUBLIC - Tags: POLITICS CIVIL UNREST)
Hoto: AFP/Getty Images

Bayan watani hudu na gawgwarmaya, daga karshe dai 'yan tawayen Seleka sun kifar da shugaba François Bozize na Jamhuriya Afrika ta Tsakiya daga karagar mulki.

Kifar da shugaba François Bozize na kama da rama wa kura aniyarta, domin shi ma ta wannan hanya ya zo karagar mulki a shekara 2003, kamin daga bisani a zabe shi ta hanyar demokradiya a shekara 2005.

A watan Disemba na shekara da ta gabata kungiyar tawayen Seleka ta shiga gwagwarmayar kifar da shugaba Bozize wanda take zargi da nakasa tattalin arzikin kasa da kuma jefa al'umma cikin halin kaka ni kayi.Saura kiris Seleka ta shiga babban birnin Bangui,amma bangarorin biyu suka shiga tattanawa a birnin Libreville na kasar Gabon, kuma su ka yi nasara rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya ranar 11 ga watan Janairun wannan shekara.

Saidai ba aje ko ina ba,'yan tawayen Seleka suka zargi shugaba François Bozize da rashin mutunta wannan yarjejeniya, domin a cewarsu ya ki belin firsinonin siyasa, sannan ya na ci gaba da rike madafin iko.Bugu da kari 'yan tawayen sun nuna rashin gamsuwa akan cigaba da zaman sojojin Afirka ta Kudu a birnin Bangui.Saboda wannan dalilai da ma karin wasu, su ka yanke shawara sake daukar makamai.Cikin kiftawa da bisimilla, suka yi nasara darkakawa har zuwa fadar shugaban kasa ba tare da fuskantar turjiya mai tsanani ba, duk kuwa da sojojin kasa da kasa da ke jibge a birnin Bangui.

François Bozizé, Präsident von Zentralafrika. President of the Central African Republic Francois Bozize attends a signing ceremony in the Great Hall of the People on Thursday, Sept. 10, 2009, in Beijing, China. (AP Photo/Feng Li, Pool)
Francois BozizeHoto: AP

Kakakin kungiyar tawayen Seleka Eric Massi yayi hira ta mussamman da sashen faransanci na DW, inda ya tabbatar da cewar sojojin kasa da kasa ba su tsoma baki ba:

"A iya sani na, babu wasu dakarun kasa da kasa da suka shiga wannan rikici.A yanzu abinda mu ka fi bada fifiko kan sa shine mun maido doka da oda,ko ina cikin kasa, hasali ma mu yaki wanda ke amfani da wannan dama domin kwasar ganima".

Banda sojojin Afirka ta Kudu, da kuma na Kungiyar Kasashen Yankin Tsakiyar Afirka, itama kasar Faransa da ta yi wa Jamhuriya Afrika ta Tsakiya mulkin mallaka, na da daruruwan sojoji, wanda ke gadin filin saukar jiragen sama na birnin Bangui.

A cewar Eric Massi shugaba Bozize kamin ya ranta cikin na kare,saida ya rarraba makamai ga magoya bayansa, domin su cin zarafin jama'a, da zumar bata sunan kungiyar Seleka.

A yayin da aka tambayi Eric Massi game da makomar hambarraren shugaban kasa, cewa yayi:

Seleka rebel coalition member, which launched a major offensive last month, hold on January 10, 2013 a position in a village 12 kms from Damara, where troops of the regional African force FOMAC are stationned. Rebels in Central Africa on March 22, 2013 were advancing on the capital Bangui after forcing their way through a key checkpoint manned by international forces, a military source told AFP. The rebels from the Seleka coalition had shot their way through the Damara checkpoint, some 75 kilometres (47 miles) north of the capital, around 1100 GMT, said a source with the Multinational Force of Central Africa (FOMAC) which was manning the roadblock. AFP PHOTO/ SIA KAMBOU (Photo credit should read SIA KAMBOU/AFP/Getty Images)
Hoto: AFP/Getty Images

" A yanzu ba ta Bozize muke ba, abinda ya fi damuwarmu shine mu tabbatar da tsaro a fadin kasa gaba daya, sannan mu sami hanyoyin fuskantar mayan kalubale da ke gabanmu.Allashi daga baya, cikin nutsuwa za mu tunani game da makomar hambarraran shugaban."

A halin da ke ciki dai yanzu rahotani daga Jamhuriya Afrika ta Tsakiya sun ce kura ta fara lafawa, saidai kowa ya shige a gidansa, sannan shaguna sun kasance a rufe.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani