1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matasa da ke cinikin kwadi a Kaduna

September 11, 2019

A wani mataki na yaki da zaman kashe wando tsakanin matasan Kaduna wasu gungun marasa aiki na yin sana’ar kamun kwadi daga rafin Kadunan wanda suke sayar da su.

https://p.dw.com/p/3POYv
Symbolbild Wort der Woche Froschperspektive
Hoto: picture-alliance/Blickwinkel/H. Schmidbauer

Matasa masu yawa ne a wata unguwar ta Kaduna da ake kira da sunan Gwari suka yi watsi da wasu kananan sana’o’in hannu da suke yi domin rungumar sana’ar kamun kwadi da suke samun makudan kudade a kowace rana. Sana’ar dai a cewar shugaban matasan Felix Peter na bunkasa a arewacin Nigeria sakamakon yadda wasu kabilun ke bukatar naman kwado da kuma yadda ake magani da bangaren jikinsa.