1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kama masu zanga-zanga a Masar

June 16, 2017

Jami'ai a Masar, sun kama wadanda suka nuna turjiya da matakain mahukuntan kasar na amincewa bai wa Saudiyya wasu tsibiran kasar. Gwamman jama'a ne dai suka shiga ragar jami'n tsaro kan wannan batu a kasar.

https://p.dw.com/p/2ep7d
Ägypten Proteste gegen die Übergabe von zwei Inseln
Hoto: Reuters/A. Dalsh

'Yan sanda a kasar ta Masar sun kama mutane da dama daga cikin gungun 'yan adawa da suka yi kira da a gudanar da zanga-zanga, bayan majalisar dokokin kasar ta kada kuri'ar amincewa da mika wa Saudiyya wasu tsibirai guda biyu. Wani lauya mai zaman kansa ya bayyana cewar mutane fiye da 50 ne aka tsare daga ranar Laraba zuwa wannan rana ta Juma'a. 'Yan adawa dai sun zargi gwamnatin Masar da mika wa Saudiyya wadanan tsibirai domin samun tallafin kudi daga kasar.

A ranar Talatar da ta gabata ma dai wasu 'yan jarida sun fito kan titunan Alkahira babban birnin kasar don nuna rashin amincewa da yarjejeniyar kafin 'yan sanda sun tarwatsa su. Tun bayan da gwamnatin Al-Sissi ta Masar ta bayyana cewar ta cimma yarjejeniya da Saudiyya a kan tsibiran biyu cikin watan Afirilu ne, zanga-zanga ta ki ci ta ki cinyewa a wannan kasa.