1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamaru: Akere na kara samun goyon baya

Salissou Boukari
January 16, 2018

'Yan adawar kasar Kamaru gami da kungiyiyoyin fararar hulla sun yi wani hadin gwiwa na goyon bayan takarar lawya Akere Muna, da ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar neman shugabancin kasar.

https://p.dw.com/p/2qwim
Akere Muna
Lawya Akere Tabeng Muna dan takarar neman shugabancin kasar KamaruHoto: picture-alliance/dpa/MAXPPP/J. P. Kepseu

A birnin Yaounde ne dai aka girka wannan tsari da aka kira tsari na sabuwar Jamhuriyar ta Kamaru, inda a bayyane suka zabi Lawya Akere Tabeng Muna, wanda yake tsohon shugaban kungiyar lawyoyin kasar ta kamaru ne a matsayin wanda zai tsaya musu takarar neman shugabancin kasar a cewar wata sanarwa da suka fitar.

Wannan tsari dai ya kumshi kananan jam'iyyun adawa guda tara, da kuma kungiyoyin fararar hulla, cikinsu har da kungiyar nan mai suna "Now" ma'ana yanzu kenan wata sabuwar kungiyar da aka kafa ta neman sauyi a kasar ta Kamaru wadda dan takarar Akere Muna ya kafa tun bayan da ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takara a watan Oktoban da ya gabata.