1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Jami'an tsaro sun hana zanga-zangar Kamaru

September 22, 2020

'Yan sanda a birnin Douala na Jamhuriyar Kamaru sun tarwatsa masu zanga-zangar kin jinin gwamnatin kasar.

https://p.dw.com/p/3irFp
Madugun Adawar Kamaru Maurice Kamto
Madugun Adawar Kamaru Maurice KamtoHoto: DW/E. Topona

Jama'a dai ta yi jerin gwano a titunan Douala, inda wasu suka rike tutar Kamaru, suna fadin kalamai munana kan gwamnatin Shugaba Paul Biya.

Tun da farko madugun adawar kasar Maurice Kamto  ya kira zanga-zangar domin matsawa gwamnati lamba ta tsagaita wuta a rikicin 'yan awaren kasar da kuma kawo sauye-sayue a hukumar zaben kasar. 

To sai dai kuma masu zanga-zangar sun sha da kyar bayan da jami'an tsaro suka watsa musu hayaki mai sa hawaye domin tarwatsa su. Kazalika akwai wasu wadanda suka shiga hannun jami'an tsaron a matsayin masu kunnen kashi.