1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamen 'yan jarida ya karu a shekara ta 2016

Gazali Abdou Tasawa
December 13, 2016

Kungiyar kare hakkin jarida ta kasa da kasa ta Reporteur Sans Frontiere ta ce adadin 'yan jarida da aka kama ko kuma ake tsare da su a kasashen duniya daban-daban ya kai 348 a shekarar 2016. 

https://p.dw.com/p/2UCgn
Symbolbild Pressefreiheit
Hoto: picture-alliance/dpa/I. Langsdon

Kungiyar ta bayyana haka ne a cikin rahoton bitar aikin jarida na shekara da ta fitar a wannan Talata inda ta ce ya zuwa yau 'yan jarida 348 ne ake tsare da su a gidajan kurkuku a fadin duniya. 

Kungiyar ta Reporteur Sans Frontiere wato RSF a takaice, ta kara da cewa adadin 'yan jaridar da ake tsare da su ya karu da kashi 22 cikin 100, ya kuma nunka har sau hudu a kasar Turkiyya, inda ake tsare da 'yan jarida sama da 100 bayan yinkurin juyin mulkin da aka yi a kasar da ya ci tura. 

Rahoton ya bayyana cewa adadin 'yan jarida mata da aka tsare ya nunka gida hudu a shekarar bana inda yanzu haka ake tsare da mata 'yan jarida 21 sabanin biyar kawai a shekarar da ta gabata.