1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Rayuka na kara salwanta

Yusuf Bala Nayaya
January 10, 2019

Hashim Abdelrahim da ke magana da yawun 'yan sanda ya ce sun yi nasara ta tarwatsa gangami na masu adawar da gwamnati ta hanyar amfani da hayaki mai sa hawaye.

https://p.dw.com/p/3BI1q
Sudan fordert al Bashir heraus
Hoto: picture-alliance

Masu zanga-zanga uku ne suka rasu bayan da 'yan sanda suka tarwatsa wani gangami na masu gangamin adawa da gwamnati a birnin Omdurman na Sudan kamar yadda 'yan sanda suka bayyana a ranar Alhamis.

A cewar Hashim Abdelrahim da ke magana da yawun 'yan sanda sun yi nasara ta tarwatsa gangami na masu adawar da gwamnati ta hanyar amfani da hayaki mai sa hawaye kasancewar gangamin nasu ya saba wa doka.

A cewar Hashim Abdelrahim dai daga bisani sun samu labari na cewa mutane uku sun rasu yayin da wasu da dama suka samu raunika amma suna ci gaba da bincike. Babu dai cikakken bayani kan yadda mutanen suka rasu cikin jawabin na jami'in 'yan sandan.