1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karfafa rundunar Minusma a Mali

Abdoulaye Mamane Amadou
September 26, 2019

Shugaba Issoufou Mouhamdou na Jamhuriyar Nijar ya ce dole a kara karfin aikin rundunar kiyaye zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a kasar Mali ta yadda za ta iya yin yaki kungiyoyin 'yan ta'adda.

https://p.dw.com/p/3QGZV
Niger Treffen der afrikanischen Union in Niamey - Mahamadou Issoufou
Hoto: AFP/I Sanogo

Shugaba Isssoufou na kalaman ne a yayin wata hira da manema labarai, inda ya kara jadadda bukatar cewa ya zama wajibi Kungiyar Tarayyar Afirka ta AU, ya zama wajibi da ta samu wakilici a kokarin kasashen duniya na samun mafita kan rikcin kasar Libiya da yaki ya daidaita.

Issoufou Mouhamadou da ke magana da yawun takwarorinsa na kasashen Sahel da na yammacin Afirka, ya kara da cewa, "rikicin Libiya ya haddasa mumunar illa ga kasashen sahel da wasu kasashen Afirka, saboda hakan ba za ta yiwu ba a kaurace kasashen na Afirka wajen magance shi", tare da nuna bukatar kafa manzo na musamman na Majalisar Dinkin Dunyia da AU a Afirka da zai wakilci bangarorin biyu.