1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karin dakaru a Jamhuriya Afirka ta Tsakiya

January 1, 2013

Kungiyar ƙasashen yankin Tsakiyar Afirka ta aika ƙarin sojoji a birnin Bagui domin kare shi daga mamayar 'yan tawaye.

https://p.dw.com/p/17C2n
Soldiers from the Republic of Congo, operating under a multinational central-african regional mandate, arrive by airplane to boost existing forces, at an airport in Bangui, Central African Republic Monday, Dec. 31, 2012. Rebels in the Central African Republic on Monday rejected appeals for them to halt their advances and to negotiate to form a coalition government. (Foto:Ben Curtis/AP/dapd)
Sojojin ƙungiyar CEEAC sun ja daga a birnin BanguiHoto: dapd

Kasashen yankin tsakiyar Afirka a wannan Talata, sun fara tura dakaru ƙasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, domin kare babban birnin ƙasar na Bangui daga faɗawa a hannun 'yan tawaye, da ke neman kawar da gwamnatin Shugaba François Bozize.

Kimanin dakaru 120 daga ƙasashen Gabon, Kongo-Brazzaville da Kamaru, sun haɗe da dakarun ƙasar Chadi 400, inda su ka ja daga, a garin Damara, wanda shi ne birnin mai mahimmaci kafin kaiwa birnin Bangui fadar gwamnati. Dakarun za su kare nausawar da 'yan tawayen da ake kira Seleka ke yi, domin hamɓarar da gwamnati.

Tun da fari shugaba Bozize ya nemi 'yan tawaye su shiga gwamnatin haɗin kan ƙasa, sannan su bar shi, ya ƙarasa wa'adinsa na mulki.

A wani labarin, an samu hargitsi a wannan Talata, a birnin na Bangui fadar gwamnati Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, inda aka zargi wani 'yan sanda da hallaka wani matashi da ake zargi da alaƙa da 'yan tawaye, kuma tashin hankalin da ya biyo baya, ya kai ga mutuwan ɗan sanda ɗaya.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Yahouza Sadissou Madobi